An raunata wani Fasto tare da kona gidaje da dama yayin da wasu fusatattun matasa Musulmi suka je neman wata mata da ta aikata sabo a jihar Bauchi.
An ce matar ta watsa wani faifan bidiyo a shafukan sada zumunta inda wani da ya Musulunta ya yi magana kan Annabin Musulunci.
Matar da ake magana a kai ma’aikaciyar gwamnati ce ’yar asalin Gombe, amma ta yi aure a karamar hukumar Warji da ke Bauchi.
Wasu fusatattun matasa ne suka je neman matar bayan sallar Juma’a a ranar Juma’a 20 ga watan Mayu, inda ba a same ta ba, sai dai ana zargin cewa sun kai farmaki inda suka lalata kadarori na mabiya addinin Kirista a yankin Katangan da ke karamar hukumar Warji a jihar Bauchi. .
Wasu Kiristoci da suka hada da wani Fasto na Cocin ECWA, sun jikkata.
Hakan na zuwa ne mako guda bayan da Deborah Samuel, dalibar kwalejin ilimi ta Shehu Shagari da ke Sokoto, ta gamu da ajalinta bayan ta zagi Annabi Muhammad (SAW).
#WARJI LGA of Bauchi state today... Alleged BLASPHEMY by a nurse. Who was said to be whisked out of the city. This resulted to burning of houses and shops. Heard there's currently a religious rioting between the Christians and Muslims there.
— JOStified 🇳🇬 (@_Thrixian) May 20, 2022
More details to come... pic.twitter.com/j3w0urwQAR
RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI