Da Duminsa: Gwamnonin APC sun shirya tsaf domin zaban dan takarar shugaban kasa


Wani rahoto da ke fitowa ya nuna cewa gwamnonin Najeriya a karkashin jam’iyyar APC sun amince da zaben fidda gwani na shugaban kasa da za a gudanar kafin babban zaben 2023.

Legit ta ruwaito cewa Joe Igbokwe, jigo a jam’iyyar APC wanda ya bayyana hakan, ya fadi a ranar Talata, 24 ga watan Mayu, cewa gwamnonin sun ba da cikakken goyon baya ga duk wani mai neman tsayawa takarar shugaban kasa domin nuna bajintarsa cikin gaskiya da adalci.

Wannan magana dai ta fito ne bayan wata tattaunawa ta sirri da gwamnonin jam’iyyar mai mulki suka yi, kamar yadda rahotanni suka bayyana a baya

"Gwamnonin APC sun bayyana goyon bayansu ga zaben fidda gwani na shugaban kasa da za a gudanar, tare da baiwa duk wani wanda ya sayi fom din tsayawa takarar shugaban kasa damar yin takara cikin gaskiya da adalci."

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN