Amarya ta yi batan dabo ranar daurin aurenta, nan take an daura aure da kanwarta a matsayin sabuwar Amarya


Wata Amarya ta bace a ranar daurin aurenta a jihar Neja, don haka aka ci gaba da daurin auren inda kanwar amaryar ta maye gurbin Amarya.

‘Yan uwan ​​ma’auratan sun hallara a ranar Juma’a, 13 ga watan Mayu, domin daurin auren a garin New Bussa da ke jihar Neja, inda suka lura cewa Amaryar ta bata.

Da aka tambayi abokan Amaryar, sun bayyana cewa Amaryar ta yi nuni da cewa za ta je wani wuri ta buya na dan wani lokaci saboda ba ta da sha’awar yin aure.

Iyalan Amarya sun yi ganawar sirri nan take inda daga bisani suka gayyaci dangin ango zuwa taron, kamar yadda jaridar Borgu Online ta ruwaito.

Iyalan biyu sun amince cewa za a ci gaba da daurin auren tare da kanwar amaryar a matsayin sabuwar Amarya.

Rahotanni sun ce kanwar ta amince ta auri Angon ‘yar uwarta kuma aka daura auren.

An ce Amaryar da ta maye gurbinta tana murna da "mijin da Allah ya ba ta."

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN