Yadda yarinya mai shekara 5 ta fuskanci wani bala'i a hannun mahaifiyarta, duba dalili


Wata mata mahaifiyar Yara biyu mai suna Tina Idoroyen ta tsoma hannun diyarta yar shekara 5 cikin zuwan zafi bisa zargin satar soyayyen kifi. Jaridar isyaku.com ya samo.

Tina tana zaune da yayanta biyu a gida mai lamba N02, Gregory Street, Ikot Ansa da ke birnin Calabar a jihar Cross River.

Tina Idoroyen tana sana'ar sayar da abinci ne. Bayanai sun ce ta soya yankan kifi gida 19 domin ta sayar tare da abincinta. Sai dai lokacin da ta dawo sai ta tarar saura kwaya daya kacal. Bayan ta gudanar da bincike ne sai ta gano cewa diyarta mai shekara 5 da haihuwa ce ta cinye kifin.

Sakamakon haka Tina ta tsoma hannun yarinyar cikin ruwan zafi wai domin ta ladabyar da ita.

Tuni dai yan karadin kare hakkin kananan yara a jihar Cross river suka fuskanci Tina sakamakon azabtar da diyarta ta hanyar kone hannayenta a cikin ruwan zafi. 

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN