Hukumar NBC ta haramta shirin 'Idon Mikiya' na tashar Vision Fm da tarar N5m


Hukumar kula da gidajen rediyo da talabijin NBC ta dakatad da haska shirin Idon Mikiya na tashar VisionFM kan laifin tattauna tsawaita nadin shugaban hukumar leken asirin kasa NIA, Rufa'i Abubakar.

A wasikar da NBC ta turawa shugaban tashar VisionFM ranar Laraba, tace ta sanyawa gidan rediyon takunkumi ne saboda illar maganganun da sukayi a shirin 'Idon Mikiya' a ranar 5 ga Junairu, 2022.

NBC tace wannan ya sabawa sashe 39 (3) (b) na kundin tsarin mulkin Najeriya da ta haramta tattauna lamuran tsaro da hukumominta.

A cewar wasika:

"Abubuwan da kuke tattaunawa, ciki har da nadi a hukumar leken asirin Najeriya (NIA) ya sabawa sashe 39 (3) (b) na kundin tsarin mulkin Najeriya, wanda ya sanya takunkumi kan abubuwan da suka shafi lamuran tsaro."

Hukumar ta ci Vision FM tarar N5 million kuma ta dakatad da shirin Idon Mikiya na tsawon watanni shida.

NBC tace ana bayyana sirrukan gwamnati a shirin kuma hakan na da illa da tsaro.

A watan Disamba, shugaba Muhammadu Buhari ya tsawaita wa'adin shugaban NIA duk da cece-kucen da akeyi.

Legit Hausa

================

Daga Jaridar iyaku.com

Reported by ISYAKU.COM

Latsa nan ka shiga Group dinmu na Whatsapp domin samun labaranmu kai tsaye

https://chat.whatsapp.com/G83TOEf1MUmDTiYaMTb02g

Domin aiko labari mu wallafa maka LATSA NAN

Domin zama Wakilinmu a garinku LATSA NAN 

Domin Korafi/Tuntubemu LATSA NAN

Shafukan sada zumunta

Twitter twitter.com/isyakulabari

Facebook fFacebook.com/isyakalabari

 

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN