Jaridar isyaku.com ya lura an yaga postocin yan takarar ne daga shataletalen Haliru Abdu zuwa titin Ahmadu Bello har zuwa shataletalen Asibitin Sir Yahaya a garin Birnin kebbi.
Sai dai rahotanni na cewa har zuwa titin Sarki Haruna da sauran sassan garin Birnin kebbi an yaga postocin.
Bincike da Jaridar isyaku.com ya gudanar, ya nuna ba hannun wata hukuma dangane da cire, yaga, ko lalata postocin yan takara na kowane irin jam'iyar siyasa a jihar Kebbi.
Sai dai wata majiya da ke da masaniya kan harkoki da halayen yan siyasa a jihar Kebbi, ya yi hasashen cewa ba mamaki yan daban siyasa na yan siyasa da ke kira da manuniya cewa a yi tashin hankali ne ke sa yan daban siyasa su aikata wannan aiki.
Isah Asalafi, Kakakin jam'iyar siyasa na jam'iyar APC reshen jihar Kebbi tsagin Gwamna Bagudu, ya ce bai da labarin aukuwar hakan a lokacin da muka tuntube shi kan lamarin.
Kazalika Umar Namashaya Diggi, Sakataren jam'iyyar APC Asali, tsagin tsohon Gwamna Adamu Aliero, ya ce basu da hannu wajen wannan aiki. Ya ce "A ko yaushe mu muna kira ne ga magoya bayan mu cewa a zauna lafiya"
================
Daga Jaridar iyaku.com
Reported by ISYAKU.COM
Latsa nan ka shiga Group dinmu na Whatsapp domin samun labaranmu kai tsaye
https://chat.whatsapp.com/G83TOEf1MUmDTiYaMTb02g
Domin aiko labari mu wallafa maka LATSA NAN
Domin zama Wakilinmu a garinku LATSA NAN
Domin Korafi/Tuntubemu LATSA NAN
Shafukan sada zumunta
Twitter twitter.com/isyakulabari
Facebook fFacebook.com/isyakalabari
Rubuta ra ayin ka