Malam Abdullahi ya ce " Duk gidana gaba daya N1.4.m aka bani, yanzu wata guda kenan da bani kudi. Ko Gwamnati bata inya Gina gida a cikin wata guda, domin ga gida can ga Gwamnati shekaru nawa bata kare su ba.
" Za mu barsu ga Allah, ba ka iya fada da Gwamnati tunda ba Gwamnatin kwarai ce ba, ba Gwamnatin adalci ce ba. Abin da ake so ga Gwamnati, ai akwai inda muke ji ana basu kudi a basu fili da isashen lokaci su yi gini.
Amma ba kudi da za su yi maka gini, ba lokaci. Yau fili kawai in kana bukata sai ka saye shi Naira miliyan daya da wani abu". Inji Malam Abdullahi
Malam Abdullahi ya ce yana da dakuna hudu a gidanshi bayan ban daki da wajen dafa abinci da haraba. Ya yi korafin cewa N1.4m da Gwamnati ta ba shi bai isa ya saye fili kuma ya yi gini a cikin wata daya ba, kafin aka gudanar da rusau da ya yi sanadin rushe gidansa.
Kalli bidiyo:
Reported by ISYAKU.COM
Latsa nan ka shiga Group dinmu na Whatsapp domin samun labaranmu kai tsaye
https://chat.whatsapp.com/G83TOEf1MUmDTiYaMTb02g
Domin aiko labari mu wallafa maka LATSA NAN
Domin zama Wakilinmu a garinku LATSA NAN
Domin Korafi/Tuntubemu LATSA NAN
Shafukan sada zumunta
Twitter twitter.com/isyakulabari
Facebook facebook.com/isyakalabari