Buhari ya yi wa Yan bindigan Sokoto mugun baki, duba abin da ya ce


Shugaban ƙasa, Muhammadu Buhari, ya jaddada kudirin gwamnatinsa na magance yan bindiga domin kare yan Najeriya daga sharrin su.

Buhari ya yi wannan furucin ne lokacin da tawagar gwamnatin tarayya ta kai ziyarar jaje ga gwamna Aminu Tambuwal bisa kisan matafiya 23 a jihar Sokoto. 

Wannan na kunshe ne a wata sanarwa da kakakin gwamnan Sokoto, Muhammad Bello, ya fitar ranar Asabar, kamar yadda daily Nigerian ta rahoto. 

Shugaban tawagar gwamnatin tarayya kuma mai bada shawara kan tsaro, Babagana Monguno, shine ya isar da sakon shugaban Æ™asa na jaje da ta'aziyya. 

Buhari ya yaba wa gwamna Tambuwal bisa datse tafiyar aiki da ya yi domin karÉ“an tawagar gwamnatin tarayya duk da ba'a sanar masa a kan lokaci ba. 

Yace: 

"Mun zo Sokoto bisa umarnin shugaba Buhari, dan jajanta maka da sauran al'umman Sokoto da kuma mai martaba sarkin Musulmi, kan abubuwa mara daÉ—i dake ta faruwa a makonnin da suka shuÉ—e."

 "Shugaban Æ™asa ya damu sosai kan yadda ake samun faruwar haka lokaci bayan lokaci, wanda ke sanadin rasa rayuwar mutanen da basu ji ba basu gani ba." 

"Kowane rai na da muhimmanci, abun na damun shugaban Æ™asa yadda mutane ke mutuwa ta hanyar rashin tausayi. Shugaba Buhari na mika ta'aziyyarsa kan yan Najeriya da suka mutu." 

Wajibi a hukunta masu hannu a kisan matafiya - Buhari

 Monguno ya Æ™ara da cewa, shugaba Buhari ya jaddada kokarin gwamnatinsa na tabbatar da an kame duk mai hannu a kisan kuma sun girbi abinda suka shuka. 

"Buhari ya ƙara jajanta lamarin tare da tabbatar da cewa an cafke duk me alaƙa da wannan kisan na rashin Imani da rashin tausayi kuma a hukunta su."

 "Shugaban Æ™asa ba ya jin daÉ—in halin da yan Æ™asa suka tsinci kansu, ya umarci dukkan hukumomin tsaro kada su huta har sai sun share baki É—aya waÉ—an nan yan ta'addan."

 "Dukkan hafsoshin tsaro suna nan, wanda hakan wata alama ce shugaban Æ™asa na kokarin shawo kan wannan lamarin." 

Yan bindiga na shigowa daga Zamfara - Tambuwal 

Da yake nasa jawabin, Gwamna Tambuwal yace a kwanan nan yan bindiga da masu garkuwa sun jefa al'ummar Sokoto cikin mawuyacin hali. 

A cewar gwamnan, luguden wutan dakarun soji na Operation Hadarin Daji a Sokoto don kawo karshen yan bindiga a Zamfara, shi ke koro su zuwa Sokoto. 

 Source: Legit 

Reported by ISYAKU.COM

Latsa nan ka shiga Group dinmu na Whatsapp domin samun labaranmu kai tsaye

https://chat.whatsapp.com/CTugsexjJhBCwuOLVzkGrg

Domin aiko labari mu wallafa maka LATSA NAN

Domin zama Wakilinmu a garinku LATSA NAN 

Domin Korafi/Tuntubemu LATSA NAN

Shafukan sada zumunta

Twitter twitter.com/isyakalabari

Facebook facebook.com/isyakalabari

 

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN