Attahiru Bafarawa tsohon Gwamnan jihar Sokoto ya barota ya ce....


Tsohon gwamnan Sokoto a arewacin Najeriya Attahiru Dalhatu Bafarawa, ya bayyana takaicinsa kan kashe-kashen al'umma da 'yan bindiga ke yi a yankin, yana mai kira ga Shugaban Ƙasa Muhammadu Buhari da "ya ji tsoron haɗuwarsa da Allah
".

Tsohoin gwamnan ya bayyana haka ne cikin wata hira da BBC Hausa kwanaki kaɗan bayan 'yan fashin daji sun ƙona wata motar bas ɗauke da mutum kusan mutum 30 a cikinta Ƙaramar Hukumar Sabon Birni ta Sokoto.

Bafarawa ya ce: "Wajibi ne Buhari ya bi al'umma a zauna a tattauna kamar yadda ya bi su gida-gida lokacin da yake neman ƙuri'a, saboda mu taimaka masa wajen haɗuwarsa da Allah."

Hare-haren na masu garkuwa da mutane na ci gaba da haddasa salwantar rayukan al'umma a yankin arewa maso yammacin Najeriya.

Lamarin ya fi ƙamari a 'yan kwanakin nan a yankin Isa da Sabon Birni na jihar Sokoto da kuma yankin Shinkafi na jihar Zamfara duk da kokarin da gwamnatin tarraya da na jihohin ke cewa suna yi.

Latsa hoton da ke ƙasa ku saurari cikakkiyar hirar:

Video content

Video caption: Ya kamata Buhari ya ji tsoron gamuwarsa da Allah - Attahiru Bafarawa

BBC Hausa

Reported by ISYAKU.COM

Latsa nan ka shiga Group dinmu na Whatsapp domin samun labaranmu kai tsaye

https://chat.whatsapp.com/CTugsexjJhBCwuOLVzkGrg

Domin aiko labari mu wallafa maka LATSA NAN

Domin zama Wakilinmu a garinku LATSA NAN 

Domin Korafi/Tuntubemu LATSA NAN

Shafukan sada zumunta

Twitter twitter.com/isyakalabari

Facebook facebook.com/isyakalabari

 

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN