Da duminsa: Yan sanda sun kama wadanda suka yi wa Minista Malami karya kan kutsen gidan Alkalin Kotun koli Mary Odili (Hotuna)


Rundunar Yan sandan Najeriya a ranar Alhamis 10 ga watan Nuwamba, ta yi faratin mutum 16 da ake zargin sun kutsa gidan wata babban Jojin Kotun koli Mary Odili a birnin Abuja.

Kakakin rundunar na kasa CP Frank Mba ya yi faratin mutanen ga manema labarai a ofishin sashen binciken manyan laifuka na Criminal Investigations Department CID a birnin Abuja.

Ya ce wadanda aka kama sun hada da wani hafsan yansanda na bogi mai suna CSP Lawrence Ajojo da kuma wasu mutum bakwai da suka tsere.

Ya ce mutanen sun kutsa gidan Jojin ne bayan sun sami Labarin cewa Jojin ta aje makuddan kudaden daloli a gidanta. 

Ya ce wadanda aka kama sun hada da wani tsohon Wakilin Jaridar Thisday Newspaper Stanley Nkwazema; da ma'aikatan Banki, Lauyoyi, Malaman tsibbu da Bokaye.


Reported by ISYAKU.COM

Domin samun labaran mu ta Whatsapp kai tsaye Latsa Link a kasa

https://chat.whatsapp.com/CTugsexjJhBCwuOLVzkGrg

Domin Tuntubar mu ko aiko Labari LATSA NAN

Domin zama Wakilinmu LATSA NAN

Shafin mu na Facebook facebook.com/isyakulabari 

Shafin mu na Twitter twitter.com/isyakulabari

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN