Type Here to Get Search Results !

Duba abin da Gwamnonin PDP suke yi a wajen taron gangamin jam'iyar a Abuja (Hotuna)


Gwamnonin babbar jam'iyyar adawa ta PDP a Najeriya sun shiga ganawar sirri a wurin babban taron jam'iyyar da ke gudana yanzu haka a Abuja.

Taron na kwana biyu, ana gudanar da shi ne a dandalin Eagle Square kuma ba za a tashi ba har sai an zaɓi shugabannin jam'iyyar a muƙamai daban-daban a mataki na ƙasa.

Tsohon Mataimakin Shugaban Ƙasa Atiku Abubakar na cikin gwamnonin da ke yin ganawar. Kazalika tsohon Gwamnan Kano Sanata Rabi'u Kwankwaso na cikin ganawar.

Tuni manya da kuma masu faÉ—a-a-ji na PDP suka cika filin taron.

Post a Comment

0 Comments
* Please Don't Spam Here. All the Comments are Reviewed by Admin.

Top Post Ad

Below Post Ad

Hollywood Movies