Yanzu yanzu: An soma shari'ar Sheikh Abduljabbar Kabara a Kano


Shafin BBC Hausa ya ruwaito cewa wata Kotun Shari'ar Musulunci da ke birnin Kano a arewacin Najeriya tana can ta soma shari'ar malamin nan na jihar Sheikh Abduljabbar Kabara.

Jami'an gidan gyaran hali ne suka kai malamin kotu da safiyar Laraba domin a soma shari'arsa a kotun wadda mai shari'a Ibrahim Sarki Yola yake jagoranta.

Ranar Juma'a 16 ga watan Yuli ne gwamnatin jihar Kano ta gurfanar da malamin a gaban kotu bisa zargin É“atanci ga addini da kuma tunzura jama'a, zargin da ya sha musantawa.

Wakilin BBC da yanzu haka yake kotun ta Kofar Kudu a birnin Kano ya ce da alama Sheikh Abduljabbar yana cikin koshin lafiya sai dai ya dan rame.

Alkali Sarki Yola ya bayar da umarnin a shiga da Sheikh Albduljabbar cikin akwatin da wanda ake kara ke tsayawa.

Aisha Mahmud ita ce ke jagorantar lauyoyin gwamnatin Kano.

A bangaren Sheikh Abduljabbar, lauyoyinsa sun hada da Sale Mohammad Bakaro, da Yahuza mohd Nura da Bashir Sabi'u, RS Abdullahi, Y I Abubakar, Zaubairu Abubakar, Ya'u Abdullahi Umar, B S Ahmad, da kuma Umar Usman.

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN