Yadda mutanen Sunday Igboho suka fara harbin jami'an DSS da bindigogi lokacin yunkurin kamashi


Jami'an tsaro na farin kaya sun yi ikirarin cewa wasu maza da suke tsammanin masu tsaron Sunday Igboho ne sun yi musayar wuta da jami'ai a yayin samamen da suka kai gidan mai assasa samar da kasar Yarabawa a Ibadan da safiyar Alhamis.

Mai magana da yawun DSS, Peter Afunanya ya sanarwa manema labarai a ranar Alhamis bayan kama mutum 13 a gidan Igboho, Channels TV ta ruwaito.

Kamar yadda Afunanya ya sanar, samamen ya biyo bayan bayanan sirri da aka samu na cewa ana tara makamai a gidan Igboho, lamarin da yasa ake samun rashin zaman lafiya a yankin kudu maso yamma.

Luguden wuta yaran Igboho suka fara mana da muka je bincike, DSS

"A yayin da muka kusanci gidansa, wasu mutum tara da ake zargin mukarraban Igboho ne sun dinga mana luguden wuta. Shida suna dauke da AK47 sauran ukun kuma da wata bindiga," Mai magana da yawun DSS yace.

"A yayin musayar wutan, mun sheke biyu yayin da muka damke sauran. Jami'inmu daya ne wani daga ciki ya harba a hannun dama. Amma yanzu ya samu taimakon likitoci kuma yana samun sauki.

"Musayar wutan da muka yi ya dauka sa'a daya, lamarin da yasa Igboho ya samu damar tserewa. A halin yanzu ana nemansa ido ruwa jallo."

An kama mutum 13 daga cikin tsagerun Igboho, 12 maza da mace daya. An samu miyagun makamai a cikin gidansa, Channels TV ta tabbatar.

Source: Legit.ng

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN