Mata masu ciki sun mutu a turmutsutsun karbar abinci a Borno


Rahotanni na cewa akalla mata 10 ne wadanda yawancinsu ko dai masu ciki ko kuma masu shayarwa suka mutu a yayin wani turmutsutsu wajen karbar abinci a garin Monguno da ke jihar Borno a arewa maso gabashin Najeriya.

Wannan mummunan haɗari ya faru ne lokacin da dubban 'yan gudun hijirar da ke sansani suka fara rububin karɓar abinci agaji da aka kai musu.

Kungiyar Red Cross ce ta rika raba abincin, wadda ta ce ba ta ji dadin abin da ya faru ba na rasa rayuka a wurin, kuma tuni ta kai kayan agaji domin taimaka wa wadanda suka ji raunuka a lokacin.

Wata majiya ta ce jami'an tsaro sun ce mutane fun firgita suna ta guje-guje bayan an harba hayaƙi mai sa hawaye a wurin domin tarwatsa taron.

Akwai sama da 'yan gudun hijira 100,000 da ke zaune a Monguno.

Kuma mafi yawansu rikicin Boko Haram ne ya raba su da muhallansu.

Rahotun BBC

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN