Wuta na tsakar ci yanzu haka a kasuwar katako da ke kan hanyar Ahiaeke a garin Umuahia a jihar Abia.
Daily trust ta ruwaito cewa rigimar ta samo asali ne bayan wani dan kasuwa ya ki ya biya harajin N18000 da hukumar karbar kudaden harajin jihar Abia ta sa kuma ya hana wasu yan kasuwa su biya.
Wani ganau ya gaya wa Daily trust cewa hukumar ta umarci wadanda basu biya ba su rufe shagunansu amma yan kasuwan suka ki.
Daga bisani yan bangan Abia vigilante service sun je kasuwar domin tilasta yan kasuwar su rufe shagunansu, sai dai lokacin da yan bangan suke kokarin tilasta yan kasuwa su rufe shagunansu.
Sai rigima ta kaure tsakanin wani dan banga da wani dan kasuwa da aka fi sani da suna "Indomie" sakamakon haka dan banga ya harbe shi da bindiga kum ya mutu.
Geamnatin jihar Abia ta yi Allah wadai da lamarin. Ta kuma umarci yansanda su gudanar da bincike kan lamarin domin zakulo wadanda suka kona dukiyar jama'a domin hukunta su.
https://chat.whatsapp.com/IM8Uuxtia6qBsdKcEszx7s
Domin aiko labari, shawara ko tuntubarmu
LATSA NAN
SHAFUKANMU NA SADA ZUMUNTA
Facebook.com/isyakulabari