Miji ya yi tafiya har shekara 2 ya bar gida mata ta sayar da yaransa 2 kan N300.000 kwatsam sai ya dawo


Rundunar yansandan jihar Ogun ta kama wata mata yar shekara 35 mai suna Blessing Ebuneku Agoro, sakamakon sayar da yaran da ta haifa su biyu masu suna Semilore Agoro mai shekara 4, da yar uwarta Deborah Agoro mai shekara 2 akan kudi Naira 300.000.

Yansanda sun ce matar ta sayar da yaran ba tare da sanin mahaifinsu ba.

Rahotun yansanda ya nuna cewa mahaifin yaran kuma mijin matar mai suna Oluwaseyi Agoro, ya yi tafiya har tsawon shekara biyu baya gida. Bayan ya dawo ne sai matarsa ta kasa yi masa bayanin inda yaransa suke. Sakamakon haka ya kai kara wajen yansanda.

Kakakin yansanda jihar Ogun, Abimbola Oyeyemi, ta ce matar ta yi bayanin cewa ta sayar da yaran a garin Port Harcourt a kan N300.0000 ga wasu ma'aurata wadanda ke matukar bukatar yara. 

Ta ce kunci da matsanancin halin rayuwa da ta shiga bayan mijinta ya tafi ya barta da yaran har tsawon shekara biyu ya sa ta yanke shawarar sayar da yaran da ta haifa masa.

Bayanai sun ce matar tana da wasu yara biyu da ta haifa ma wani miji kafin mijinta na yanzu.

Yansanda sun kama ma'auratan da suka saye yaran, kuma suna fuskantar bincike a sashen CIID na Shelkwatar yansandan jihar Ogun.

Reported by ISYAKU.COM

Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp 
https://chat.whatsapp.com/L2WpsKOTg5Q6ieoYKEWxeB

Domin aiko labari, shawara ko tuntubarmu 
LATSA NAN 

SHAFUKANMU NA SADA ZUMUNTA 

Facebook.com/isyakulabari 


Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN