Kebbi: Yan bindiga sun farmaki kauyukan kananan hukumomin Ngaski da Shanga sun tafka ta'asa


Yan bindiga sun farmaki Gundumar Kambuwa a karamar hukumar Ngaski da wasu kauyuka a karamar hukumar Shanga suka kora shanayen bayin Allah da ba a tantance yawansu ba kawo yanzu.


Shafin ISYAKU.COM ya samo cewa da tsakiyar ranar Talata 1 ga watan Yuni yan bindigan suka farmaki garuruwan Maburo, Shagiya, Arabu lafiya, Daban kurege, da Tungan hantsi.

Rahotanni sun ce jama'a sun kaurace wa gidajensu a Kambuwa da Bunu kuma suka sami mafaka a kauyen Kimo. Kawo yanzu dai babu cikakken kididdigan irin ta'asar da Yan bindigan dajin suka aikata a kauyukan da suka kai farmaki.

Sai dai wata majiya ta tsaro mai tushe a jihar Kebbi, ta tabbatar da cewa Yan bindigan daji sun farmaki Kambuwa a karamar hukumar Ngaski da wasu kauyuka a karamar hukumar Shanga ranar Talata 1 ga watan Yuni, suka kora shanayen jama'a daga bisani suka tafi.

Rahotun Abdullahi Musa, Isyaku Garba Zuru.

Reported by ISYAKU.COM

Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp 
https://chat.whatsapp.com/IM8Uuxtia6qBsdKcEszx7s

Domin aiko labari, shawara ko tuntubarmu 
LATSA NAN 

SHAFUKANMU NA SADA ZUMUNTA 

Facebook.com/isyakulabari 


Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN