Dalibin aji karshe ya shigar da jami'a kotu bayan an koreshi don ya zagi gwamna a Facebook


Wani dalibin Najeriya mai suna Iniobong Ekpo, ya shigar da jami'ar jihar Akwa Ibom kotu kan korarsa da tayi kan abin da ya daura a kafar ra'ayi da sada zumunta na suka gwamnan jihar, Udom Emmanuel.

A cewar Soaznews Etv, jami'ar ta bayyana korar dalibin a wasikar da ta aike ranar 9 ga Afrilu, 2021 saboda rashin da'ar da ya yi. Hakazalika tace wannan ya sabawa dokar jami'ar.

Rijistarn jami'ar Joh E Udo, wanda ya rattafa hannu kan wasikar ya kara da cewa an haramtawa dalibin shiga jami'ar.

Yanzu haka ya shigar da jami'ar kotu kuma ya bukaci a biyashi kudi N20m, kuma a rabu da shi ya cigaba da karatunsa.

Abinda dalibin da daura a Facebook

Premium Times ta ruwaito cewa dalibin wanda ke karatu a tsangayar injiniyancin aikin noma ya tuhumci gwamnan da laifin rashin cika alkawarin da yayi daliban da aka yaye a 2017.

Yace:"

Shekaru biyu da kwanaki 166 bayan alkawarin da yayi, har yanzu babu ko mutum guda cikin daliban da aka yaye da ya samu ko Naira guda duk da cewa wadanda suka fita da 1st Class sun je ofishinsa amma basu gansa ba."

Source: Legit

https://youtu.be/xRYphqBjqwc

Reported by ISYAKU.COM

Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp 
https://chat.whatsapp.com/L2WpsKOTg5Q6ieoYKEWxeB

Domin aiko labari, shawara ko tuntubarmu 
LATSA NAN 

SHAFUKANMU NA SADA ZUMUNTA 

Facebook.com/isyakulabari 


Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN