Yan sanda a jihar Jigawa sun cafke wata mata mai shekara 25, Hadiza Musa kan zargin aikawa da mijinta barzahu.
Kakakin rundunar ‘yan sanda ASP Lawan Shiisu Adam ya tabbatar da kamun kamar yadda jaridar Daily Post ta ruwaito.
Ya ce lamarin ya faru ne a yammacin ranar Talata a kauyen Maradawa da ke karamar hukumar Kazaure.
Sashin Hausa na BBC ma ta ruwaito cewa rundunar yan sandan ta ce ta fara gudanar da bincike kan matar da ake zargin ta aikata wannan laifin bayan wata hatsaniya ta barke a tsakaninsu.
Adam ya ce wanda abun ya cika da shi ya samu rauni a kansa wanda hakan ya yi sanadiyyar mutuwarsa.
Ya ce an kai mamacin babban asibitin Kazaure inda aka tabbatar da cewa ya mutu.
Source: Legit
https://chat.whatsapp.com/L2WpsKOTg5Q6ieoYKEWxeB
Domin aiko labari, shawara ko tuntubarmu
LATSA NAN
SHAFUKANMU NA SADA ZUMUNTA
Facebook.com/isyakulabari