Da Ɗuminsa: Yan Bindiga Sun Sace Wani Hakimi da Matansa 2 a Jihar Neja


Wasu yan bindiga sun yi awon gaba da Hakimin Zungeru a jihar Neja tare da matansa biyu ranar Lahadi, kamar yadda dailytrust ta ruwaito.

An ɗauke Musatapha Madaki (Madakin Zungeru) tare da matan sa biyu da yammacin ranar Lahadi bayan wasu yan bindiga aƙalla 20 sun kutsa gidansa dake tsakiyar garin Zungeru.

Yan bindigan sun aje abun hawan su tsawon mita 500 da gidan hakimin, suka ƙarisa da kafafuwansu.

Maharan sun tafi kai tsaye zuwa gidan madakin, suka kutsa kai ɗakinsa suka fito dashi tare da matarsa ɗaya mai suna, Habiba.

Sun kuma yi awon gaba da matarsa ta biyu duk a wannan harin wanda maƙwabtan hakimin suka ce ya ɗauki kusan rabin sa'a ba tare da an kawo ɗauki ba.

Wannan na zuwa ne mako ɗaya bayan wasu yan bindiga sun kutsa cikin Islamiyyar Salihu Tanko dake Tegina, ƙaramar hukumar Rafi, inda suka sace ɗalibai 156.

Legit.ng hausa ta gano cewa tsakanin Zungeru da garin Tegina bai wuce tafiyar kilomita 30 ba kacal.

Source: Legit.ng

Reported by ISYAKU.COM

Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp 
https://chat.whatsapp.com/IM8Uuxtia6qBsdKcEszx7s

Domin aiko labari, shawara ko tuntubarmu 
LATSA NAN 

SHAFUKANMU NA SADA ZUMUNTA 

Facebook.com/isyakulabari 


Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN