Da Ɗumi-Ɗumi: MTN, Airtel, Glo Sun Rufe Damar Shiga Twittter a Najeriya


Kamfanonin sadarwa a Najeriya kamar MTN, Glo, Airtel da 9mobile sun fara rufe amfani da damar shiga dandalin sada zumunta twitter, kamar yadda Punch ta ruwaito.

Kamfanonin sun ce sun samu saƙon umarni daga hukumar sadarwa ta ƙasa NCC cewa su tsayar da damar shiga twitter a ƙasa biyo bayan umarnin gwamnatin tarayya na dakatar da shafin.

Yan Najeriya masu amfani da twitter sun wayi garin ranar Asabar ba tare da samun damar amfani da shafinsu na twitter ba, yayin da wasu ke amfani da wata manhajar sadarwa domin shiga shafin su.

Kamfanonin sadarwar Najeriya baki ɗaya sun bayyana ƙarƙashin ƙungiyar su cewa sun fara dakatar da damar amfani da twitter a wani jawabi da suka fitar ranar Asabar.

Jawabin wanda a ka yiwa take da "Umarnin dakatar da mafani da twitter a Najeriya" wanda shugaban ALTON, Gbenga Adebayo, da sakatarensa, Gbolahan Awonuga, suka sanya wa hannu.

Wani sashin jawabin yace: "Mu, Ƙungiyar kamfanonin sadarwa ALTON, mun tabbatar da mambobin mu sun samu umarni daga NCC cewa su dakatar da bayar da damar amfani da twitter."

"Mambobin mu sun yi biyayya ga umarnin da hukumar sadarwa NCC ta basu, kuma zasu cigaba da biyayya ga dukkan umarnin da hukumomi da masu faɗa aji suka basu a Najeriya."

A wani labarin kuma

Source: Legit

Reported by ISYAKU.COM

Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp 
https://chat.whatsapp.com/IM8Uuxtia6qBsdKcEszx7s

Domin aiko labari, shawara ko tuntubarmu 
LATSA NAN 

SHAFUKANMU NA SADA ZUMUNTA 

Facebook.com/isyakulabari 


إرسال تعليق

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

أحدث أقدم

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN