Daya daga cikin mambobin kwamitin duba wata na majalisar koli ta shari'ar Musulunci a Najeriya, Simwal Usman Jibril, ya bayyana cewa wadanda sukayi ikirarin sun ga wata jiya kuskure suka yi.
Simwal ya yi bayanin cewa ko a yau 30 ga watan Ramadana ba zai yiwu a ga watan ba saboda wasu dalilai.
Ya bayyana hakan a shafinsa a Facebook da Tuwita.
A cewarsa, hasali ya kamata jama'a suga wata ranar 30 ga wata cikin sauki amma tunda awanni jinjirin watan bai wuce 22 ba, ba za'a gani cikin sauki ba.
Ga bayaninsa: "Hasali a ranar 30 ga watan akan ga jinjirin wata cikin sauki kuma babba. Watan na fadi ne akalla waw guda daya bayan faduwar ranar idan jinjirin wata ya bayyana a jiya."
"Amma saboda sai bayan karfe 8 na daren jiya jinjirin wata ya bayyana, Insha Allah da yamman nan awanni jinjirin watan 22 kuma zai fadi bayan mintuna 42 da faduwar rana Insha Allah amma ba za'a iya gani cikin sauki ba."
"Yanzu na gama tabbatar daga kwamitin duban wata da fadar mai martana Sarkin Musulmi cewa babu inda aka ga wata a yau a Najeriya. Ko wadanda suka ce sun gani jiya sun ce basu gani yau ba," Ya kara
"Mun bayyana karara cewa da kamar wuya a ga watan yau saboda awanni jinjirin watan 22 da yan kai. Ko wadanda suka yi ikirarin gani jiya sun gaza gani yau. Hakan na tabbatar da cewa kuskure sukayi jiya."
Source: Legit
https://chat.whatsapp.com/IM8Uuxtia6qBsdKcEszx7s
Domin aiko labari, shawara ko tuntubarmu
LATSA NAN
SHAFUKANMU NA SADA ZUMUNTA
Facebook.com/isyakulabari