Musulmi Ya Sake Ɗarewa Kujerar Magajin Garin Landan Bayan Lashe Zaɓe


Sadiq Khan, musulmi na farko da ya taɓa riƙe muƙamin magajin garin Landan ya sake komawa kujerarsa a karo na biyu..

Rahoton BBC ya bayyana cewa Sadiq Khan ya sake komawa kan kujerar sa ne bayan doke abokin takararsa, Shaun Bailey, na jam'iyyar Conservative.

Khan ya samu nasara da kashi 55.2% yayin da ya kayar da abokin takarar sa Baily wanda ya samu 44.8% a zagaye na biyu na zaɓen da aka gudanar.

Sadiq Khan wanda tsohon dan majalisa ne, shine musulmi na farko da ya fara lashe zaɓen magajin garin Landan a shekarar 2016, ya kuma sake komawa kujerarsa a karo na biyu.

Khan yace: "Nayi matuƙar farin ciki da irin amincewar da mutanen Landan suka mun na in sake jagorantar birnin da yafi kowanne a faɗin ƙasa."

"Na yi alƙawarin zan yi amfani da kowacce irin dama da nike da ita wajen kawo kyakkyawan cigaba a Landan bayan wannan annobar da muke fama da ita ta shuɗe."

Source: Legit Nigeria


Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp 
https://chat.whatsapp.com/IM8Uuxtia6qBsdKcEszx7s

Domin aiko labari, shawara ko tuntubarmu 
LATSA NAN 

SHAFUKANMU NA SADA ZUMUNTA 

Facebook.com/isyakulabari 


Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN