Hotunan yadda dan shekara 23 ya auri yar siyasa mai shekara 45 a jihar Arewa


Matashi dan Najeriya mai shekaru 23 mai suna Adam Dalla ya aura fitacciyar 'yar siyasa a Adamawa mai suna Barista Jamila Babuba.

Kamar yadda wallafar da shafin @lindaikejiblogofficial yayi a Instagram, ma'auratan sun angwance a ranar 18 ga watan Mayun 2021 kuma zasu yi walimar aurensu ne a ranar 31 ga watan Mayun 2021.

Kyawawan hotuna da katin gayyatar liyafar bikin sun bazu a kafafen sada zumunta kuma jama'a sun matukar nuna sha'awarsu da wannan soyayya dake tsakanin ma'auratan.

A yayin martani ga wallafar, wata ma'abociya amfani da Instagram mai suna @ju_sapphire ta rubuta: "Gareku maso son kirgar shekaru, ku cigaba da kirgawa. Zaku iya zuwa nawa nima. Shekaru ba komai bane, natsuwa ce kawai! Duk inda ka samu soyayya, je ka ka samu farin ciki. Ba zamu dawwama a duniya ba, don haka kayi rayuwa cike da morewa. Mutane zasu yi magana, amma waye ya damu."

@jagun_of_afrika kuwa tsokaci yayi da: "Ina taya ku murna... Natsuwa da farin ciki yafi maganganun jama'a"

@mavwills6 cewa tayi: "Anya wannan yaron, ko dai bashi da iyaye ne??"

@kokolet_natural cewa tayi: "Soyayya a Ethiopia, ina taya ku murna."

Source: Legit.ng

Reported by ISYAKU.COM

Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp 
https://chat.whatsapp.com/IM8Uuxtia6qBsdKcEszx7s

Domin aiko labari, shawara ko tuntubarmu 
LATSA NAN 

SHAFUKANMU NA SADA ZUMUNTA 

Facebook.com/isyakulabari 


Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN