Da duminsa: Labarin kashe Shekau, jami'an tsaron Najeriya sun shiga shirin ko ta kwana


Jami'an tsaron Najeriya sun shiga shirin ko ta kwana sakamakon rahotannin kashe shugaban Boko Haram Abubakar Shekau.

Da yammacin ranar Laraba, an sami rahotannin da ke nuna cewa an kashe Shekau lokacin da ake gwabza fada tsakanin ISWAP da Boko Haram a dajin Sambisa. Kungiyoyin biyu sun dade basu ga maciji da juna a mazauninau da ke yankin tafkin Chadi.

Sai dai wani rahotun sirri da Jaridar Daily Trust ta sami gani, ya ce wani Kwamandan ISWAP mai suna Baana Duguri ya ce mayakan ISWAP da na Shekau sun gwabza fada ranar Laraba.

Ya ce mayakan ISWAP sun dade suna neman kama Shekau da ransa, amma Shekau ya kashe kansa da kansa bayan ya ta da bam da ke hannnunsa kuma ta tashi da shi ya mutu domin kada a kama shi da ransa.

Har yanzu hukumomin soji basu ce komi ba dangane da zancen kashe Shekau. Sai dai wata babban majiyar tsaro ta gaya wa Jaridar Daily Trust cewa an tabbatar da ikirarin ISWAP na mutuwar Shekau.

Rahotanni sun ce hukumomin soji da na DSS suna aiki kan tantance hakikanin gaskiyar ikirarin ISWAP na kashe Abubakar Shekau shugaban kungiyar Boko Haram. 

Abukakar Shekau ya dare ragamar shugabancin kungiyar Boko Haram ne a shekarar 2009 bayan kashe wanda ya kirkiro kuma ya assasa kungiyar Boko Haram Muhammed Yusuf.


Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp 
https://chat.whatsapp.com/IM8Uuxtia6qBsdKcEszx7s

Domin aiko labari, shawara ko tuntubarmu 
LATSA NAN 

SHAFUKANMU NA SADA ZUMUNTA 

Facebook.com/isyakulabari 


Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN