Type Here to Get Search Results !

Pantami: Malaman Addinin Kirista Sun Yi Tattaki Na Nuna Goyon Baya a Abuja


Kungiyar malaman addinin kirista na 'Forum of Christian Bishops and Clergy Council' ta nuna goyon bayan ta ga gwamnatin Shugaba Muhammadu Buhari kan matsayarta game da zargin da ake yi wa ministan Sadarwa da tattalin arziki na zamani, Dr Isa Ali-Pantami.

Kungiyar ta sanar da hakan ne yayin wani tattaki na goyon baya da ta yi a Unity Fountain Abuja, inda ta ce wadanda ke zargin wasu tsirarai ne a kasar da basu son sauye-sauyen da ministan ke yi.

Malaman addinin na kirista sun fito rike da takardu masu rubutu da ke nuna goyon baya da ga gwamnatin Buhari da rokonsa ya cigaba da hada kan yan kasa.

Har wa yau, kungiyar ta ce ta yi tattakin ne na zaman lafiya domin jadada bukatar zaman lafiya da hadin kai a kasa.

Bishop Abel King, jagoran masu tattakin ya ce ya zama dole su fito su bayyana matsayarsu saboda irin zargin da ake yi wa Mr Pantami.

"Shugaban kasa bisa hikimarsa ya nuna cewa Nigeria ne ke gabansa kuma zai cigaba da hada kanmu sannan ba zai bari masu son kai su rude shi ba ko tilasta shi," wannan abin yabo ne in ji Bishop Abel.

Bishop Abel ya cigaba da cewa ya kamata mutane su dena la'akari da banbancin addini, kabila ko yanki idan za su dauki mataki sai dai su mayar da hankali kan abin da zai kawo cigaba a kasa.

Kazalika, ya gargadi mutane kan furta kalaman da ka iya tada zaune tsaye a kasar.

Source: Legit


Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp 
https://chat.whatsapp.com/IM8Uuxtia6qBsdKcEszx7s

Domin aiko labari, shawara ko tuntubarmu 
LATSA NAN 

SHAFUKANMU NA SADA ZUMUNTA 

Facebook.com/isyakulabari 


Post a Comment

0 Comments
* Please Don't Spam Here. All the Comments are Reviewed by Admin.

Top Post Ad

Below Post Ad

Shiga group dinmu na WhatsApp domin samun labaran mu kai tsaye LATSA NAN
Domin zama Wakilin mu a garin ku LATSA NAN
Domin aiko Sako/Labari/Korafi LATSA NAN
Domin samun labaran mu a Facebook LATSA NAN
Domin samun labaranmu a Twitter LATSA NAN