Gwamnan jihar Kebbi Abubakar Atiku Bagudu ya ce gwamnatinsa za ta ci gaba da taimakawa mata domin idan ka gina mata tamkar ka gina al'umma ne maki daya.
Bagudu ya fadi hakan ne cikin wata sanarwa da mataimakinsa na musamman kan harkokin yada labarai Yahaya Sarki ya fitar, yana ruwaito cewa Bagudu ya ce "Yawan taimakon da za mu iya bai wa mata yanayin yadda al'umarmu za ta habaka".
Bagudu ya bayyana mata a matsayin wadanda duk wahalar da aka sha ta annobar korona ta matsin tattalin arziki ta kare a kansu.
Gwamnan ya bayyana haka ne a wajen wata makala da jihar ta shirya wa mata domin zuwan watan Ramadana, wadda aka yi wa taken "Muhimmiyar rawar da mata za su iya taka wa a Musulunci."
Makalar da aka yi ta mayar da hankali ne kan yadda mata za su tafiyar da gida a lokacin annobar korona, wajibin da ke kan mata na kula da iyali a yayin matsin tattalin arziki da kuma yadda za a kawo karshen cin zarafin mata.
Rahotun BBC Hausa
https://chat.whatsapp.com/Cw2uhGNZiIzGM88PV4gpOI
Domin aiko labari, shawara ko tuntubarmu
LATSA NAN
SHAFUKANMU NA SADA ZUMUNTA
Facebook.com/isyakulabari
RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI