Type Here to Get Search Results !

Matar da ta yi waƙar 'Mai daraja Annabi Ma'aiki' ta rasu


Allah ya yi wa Sayyada Rabi'atu Harun, matar da ta yi fiice wajen wakokin yabon Manzon Allah, Annabi Muhammad (SAW) ta riga mu gidan gaskiya. Jaridar legit ta ruwaito.

BBC ta ruwaito cewa mijinta, Sharif Mu'az ya ce ta rasu ne a ranar Talata 16 ga watan Maris a Rigasa Kaduna bayan jinya na makonni uku.

An yi jana'izarta bisa koyarwar addinin musulunci a yammacin ranar Talata kamar yadda mijinta ya bayyana.

Sharif Mu'az ya ce ya yi matkukar girgiza sakamakon rasuwar matarsa da ya bayyana a matsayin mutumiya mai hali na gari kana ya yi addu'ar Allah ya jikanta da rahama.

Marigayiyar ta rasu ta bar 'ya'ya biyu a duniya.

Cikin wakokin da ta yi na yabon annabi akwai 'Mai daraja Annabi Ma'aiki', Zahra'u Fadima, Shukriyya Sajida, Sayyidin Nasi Karimi da sauransu.

Jama'a da dama masu son wakokinta da sauran musulmi sun yi jimamin rasuwarta a dandalin sada zumunta inda suka yi addu'ar Allah ya jikanta da rahama ya gafarta mata.

Wani mai amfani da shafin Twitter Isa Usman ya yi alhinin rasuwar Sayyada Rabi'atu yana mai addu'ar Allah ya jikanta ya yi mata rahama ya karbi bakuncinta domin darajar Annabi Muhammadu Rasulullah.


Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp 
https://chat.whatsapp.com/Cw2uhGNZiIzGM88PV4gpOI

Domin aiko labari, shawara ko tuntubarmu 
LATSA NAN 

SHAFUKANMU NA SADA ZUMUNTA 

Facebook.com/isyakulabari 


Post a Comment

0 Comments
* Please Don't Spam Here. All the Comments are Reviewed by Admin.

Top Post Ad

Below Post Ad

Shiga group dinmu na WhatsApp domin samun labaran mu kai tsaye LATSA NAN
Domin zama Wakilin mu a garin ku LATSA NAN
Domin aiko Sako/Labari/Korafi LATSA NAN
Domin samun labaran mu a Facebook LATSA NAN
Domin samun labaranmu a Twitter LATSA NAN