Kebbi: Yan bindiga sun sace matan Dagacin Mussuru a garin Bena su 2 da mutum 3



Yan bindiga sun farmaki kauyen Mussuru a karamar hukumar Danko-Wasagu suka sace mutane 5 suka raunata mutum biyu da misalin karfe 11 na dare ranar Juma'a.

Wannan Yana faruwa ne a karo na biyu kasa da mako daya bayan yan bindiga sun sace wata matar aure a kauyen na Mussuru

Mussuru na iyaka da karamar hukumar Maru a jihar Zamfara, kuma tana karkashin Mazabar Dan Umaru a garin Bena da ke karamar hukumar Danko-Wasagu a jihar Kebbi.

Majiyarmu ta yi zargin cewa Yan bindigan sun sace mutum 5. Mata guda 3 da maza guda 2, Cikin wadanda aka sace har da matan Dagacin garin su 2, kuma suka raunata mutum 2.

Wadan da ake zargin an sace su ne:

1 Rashida Ahmed Maiunguwa
2 Shafa'atu Ahmed Maiunguwa
3 Hannatu Abdullahi
4 Danlami Sale
5 Hamidu Dadi

Wadanda aka raunata:

1 Ummaru Danbaba
2 Mamuda.

Yanzu haka wadanda aka raunata suna jinya a babban Asibitin garin Bena inda ake rade radin cewa watakila a turasu zuwa Assibitin UDUTH da ke Sokoto.

Majiyar mu ta yi zargin cewa Yan sanda guda biyu da ke kauyen Mussuru sun kasa iya fuskantar Yan bindigan da suka zarce su a yawa..


Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp 
https://chat.whatsapp.com/HUEzyk9QvHZ6kSk4bH2U6K

Domin aiko labari, shawara ko tuntubarmu 
LATSA NAN 

SHAFUKANMU NA SADA ZUMUNTA 

Facebook.com/isyakulabari 


Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN