Wasu da ake zargin yan fashi ne sun kashe wata mata bayan ta zari kudi N200.000 daga Banki ta shiga Keke napep a Birnin Warri na jihar Delta ranar Litinin 15 ga watan Fabrairu.
Wani ganau ya ce matar mai suna Felicia, ta zaro N200,000 ne daga Banki, sai ta tare Keke napep ta shiga, amma bayan yar tafiya, sai wadanda ke cikin Keke napep suka harbe ta da bindiga a kafa, suka kwace mata kudin kuma suka turota kasa suka gudu.
Mun samo cewa an garzaya zuwa Asibiti da Filicia, sai dai Likita ya tabbatar da mutuwarta lokacin da aka isa da ita Asibitin.
DAGA ISYAKU.COM
https://chat.whatsapp.com/HUEzyk9QvHZ6kSk4bH2U6K
Domin aiko labari, shawara ko tuntubarmu
LATSA NAN
SHAFUKANMU NA SADA ZUMUNTA
Facebook.com/isyakulabari