An kashe tsohuwa mai shekara 98 aka kwace mata wayar salula


An kashe wata tsohuwa mai shekara 98 a Duniya mai suna Oyibo Ogidi a Ovoko, da ke karamar hukumar Igbo-Eze ta kudu a jihar Enugu.

An gano gawarta ne sakamakon wari da ta fara yi bayan ta fara rubewa a gidanta da ke Amafor ranar Talata 9 ga watan Fabrairu.

Da ga dan ga uwanta Mai suna Onyeka, ya shaida wa Jaridar Vanguard cewa ba a ganta ba tun ranar Juma'a 5 ga watan Fabrairu bayan ta je ta gaida wani danuwanta a makwabta sakamakon rashin lafiya.

Onyeka ya ce wadanda suka kasheta sun caka mata wuka ne a wuya, kuma suka rufe gawarta da zanenta, daga bisani suka sace mata wayar salula da ababen amfani a cikin dakin suka gudu.






Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp 
https://chat.whatsapp.com/HUEzyk9QvHZ6kSk4bH2U6K

Domin aiko labari, shawara ko tuntubarmu 
LATSA NAN 

SHAFUKANMU NA SADA ZUMUNTA 

Facebook.com/isyakulabari 


Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN