An kashe wata tsohuwa mai shekara 98 a Duniya mai suna Oyibo Ogidi a Ovoko, da ke karamar hukumar Igbo-Eze ta kudu a jihar Enugu.
An gano gawarta ne sakamakon wari da ta fara yi bayan ta fara rubewa a gidanta da ke Amafor ranar Talata 9 ga watan Fabrairu.
Da ga dan ga uwanta Mai suna Onyeka, ya shaida wa Jaridar Vanguard cewa ba a ganta ba tun ranar Juma'a 5 ga watan Fabrairu bayan ta je ta gaida wani danuwanta a makwabta sakamakon rashin lafiya.
Onyeka ya ce wadanda suka kasheta sun caka mata wuka ne a wuya, kuma suka rufe gawarta da zanenta, daga bisani suka sace mata wayar salula da ababen amfani a cikin dakin suka gudu.
https://chat.whatsapp.com/HUEzyk9QvHZ6kSk4bH2U6K
Domin aiko labari, shawara ko tuntubarmu
LATSA NAN
SHAFUKANMU NA SADA ZUMUNTA
Facebook.com/isyakulabari