Wata mota kirar Marsandi (Mercedes) wacce ke dauke da alamar mai koyon tuki, ta bi ta kan wasu yara guda shida kuma ta murkushe su har lahira nan tà ke.
Lamarin ya faru ne ranar 16 ga watan Janairu a garin Arue-Uromi, da ke karamar hukumar Esan-North East a jihar Edo.
Isyaku.com ya sà mo cewa motar ta yi kokarin kauce wa rami ne, sai ta kwace wa direban da ke koyon tuki ta bi ta kan yaran guda shida da suke buga kwallon kafa kuma ta kashe su nan take.
Kwamandan FRSC na jihar Edo Henry Benamaisia ya tabbatar da faruwar lamarin a wata takarda da ta fito daga ofishinsa kan lamarin ga manema labarai.
DAGA ISYAKU.COM
https://chat.whatsapp.com/LKeYYgwzLbW8DdHbjNuEos
Domin aiko labari, shawara ko tuntubarmu
LATSA NAN
SHAFUKANMU NA SADA ZUMUNTA
Facebook.com/isyakulabari