Legit.ng Hausa ta fahimci cewa gwamnan Ondo, Rotimi Akeredolu, ya bada wa’adin mako daya ga makiyaya su bar kungurumin jejin da ke cikin jiharsa.
Mai girma gwamnan Ondo ya bada wannan wa’adi ne a yankurin da yake yi na kawo karshen matsalar garkuwa da mutane da sauran ta’adin da ake yi a jihar.
Sanarwar Rotimi Akeredolu ta fito ne kai tsaye a shafinsa na Twitter, a ranar Litinin 18 ga watan Junairu. 2021.
Rotimi Akeredolu a jawabin na sa yake cewa an maida jejin jihar Ondo wuraren tafka ta’adi, don haka a matsayinsa na gwamna ya dauki wannan mataki a yau.
Yace: “A yau, mun dauki babban mataki na kawo karshen matsalar garkuwa da mutane, da sauran danyen ayyukan da ake yi da muka samu labari a rahotonmu.
“Ana alakanta wadannan munanan abubuwa da wasu miyagu da ke fakewa da sunan makiyaya.” Inji gwamnan.
“Wadannan miyagu sun maida jejinmu wuraren ajiye wadanda suka yi garkuwa da su, suna tattauna yadda zasu karbi kudin fansa da yin sauran laifuffuka.”
Daga cikin matakan da aka dauka, za a bar duk wasu jeji nan da kwana bakwai. An kuma haramta kiwo da dare, sannan an hana dabbobi yawo a manyan tituna.
Gwamna ya kuma hana kananan yara kiwo, sannan bayan wannan wa’adin ya cika, gwamnati za ta bada damar duk mai bukatar yin kiwo, ya yi rajista da hukuma.
A yau ne kuma muke samun labari cewa hedikwatar tsaro cewa ‘yan bindigan da ke ta’adi a Zamfara, sun gane ba su da wayau a hannun dakarun sojojin kasa.
Janar John Enenche ya ce dakarun Sojoji sun yi wa ‘Yan bindiga rugu-rugu a dajin Zamfara.
Sojojin Najeriya na Operation Hadarin Daji sun kashe tsageru 35 a dajin yankunan Bungudu da Muradun a jihar Zamfara, har sun karbe wasu dabbobi da aka sace.
Source:
https://chat.whatsapp.com/LKeYYgwzLbW8DdHbjNuEos
Domin aiko labari, shawara ko tuntubarmu
LATSA NAN
SHAFUKANMU NA SADA ZUMUNTA
Facebook.com/isyakulabari