Karya ne, bamu kara farashin wutan lantarki ba, hukumar NERC


Hukumar lura da wutan lantarkin Najeriya NERC, ta karyata rahoton cewa ta kara farashin wutan lantarki na kashi 50 kan abinda kwastamomi ke biya yanzu a fadin tarayya.

NERC a shafinta na Tuwita ta bayyana cewa har yanzu bata bada umurnin kara farshin wuta ba kamar yadda kafafen yada labarai ke watsawa.

"Hukumar (NERC) ta samu labarin wallafe-wallafe da ake yadawa a kafafen yada labarai inda ake fadawa mutane cewa hukumar ta kara farashin wutan lantarki da 50%," hukumar tace.

"Hukumar na mai bayyana cewa babu wanda ya bada umurnin kara farashin wutan lantarki da 50% a umurnin da ta baiwa kamfanonin raba wutan lantarki a ranar 1 ga Junairu, 2021."

"Saboda haka, muna kira ga kamfanonin jarida su janye abubuwan da suka wallafa."


Source: Legit


Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp
https://chat.whatsapp.com/J9zhUeQqg52KIxyFnYByJN

Domin aiko labari, shawara ko tuntubarmu
LATSA NAN

SHAFUKANMU NA SADA ZUMUNTA

Facebook.com/isyakulabari


Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN