Wata ma'abociyar amfani da kafar sada zumuntar zamani mai suna Ngozi ta bar mutane da abun mamaki a labarin da ta bada.
A wasu jerin wallafar da tayi, Ngozi ta bada labarin yadda rikici ya barke bayan ango ya harzuka kan cewa danginsa basu samu abincin biki ba.
Amarya ta fusata bayan angon ya yi mata ihu tare da tsawa a gaban kowa. Ta je bashi hakuri tare da yi masa bayani amma sai ya fusata ya yi mata tsawa a gaban kowa.
Ngozi ta bada labarin yadda amaryar ta yi shiru tare da komawa mazauninta.
Amma kuma lokacin tafiya yana yi amarya tace wa ango ta fasa auren. A maimakon yayi kokarin gyarawa, sai yace shima ya fasa auren.
Ngozi ta wallafa: "A karshe dai amarya da dangin ango sun samu rikici. Kowa ya kama gabansa har da ango da amarya."
Wallafar da tuni ta karade kafafen sada zumuntar zamani ta janyo cece-kuce daga jama'a.
Wasu sun Dora wa amarya laifi yayin da wasu suka ga laifin ango. Wasu kuwa cewa suka yi ango ya birgesu da bai tsaya wani ja-in-ja ba, shima yace ya fasa.
A wani labari na daban, a halin yanzu, majalisar wakilai bata da bukatar ganawa da Shugaban kasa Muhammadu Buhari domin tattaunawa a kan matsalar tsaro da ya addabi fadin kasar nan, jaridar The Nation ta tabbatar da hakan a ranar Asabar.
Shugaban majalisar kamar yadda majiyoyi suka tabbatar, ya gano cewa gayyatar farko ta koma ta kabilanci da siyasa.
An gano cewa wasu 'yan majalisar da suka assasa gayyatar shugaban kasa Muhammadu Buhari sun bai wa fadar shugaban kasan hakuri.
Source: legit
https://chat.whatsapp.com/
Domin aiko labari, shawara ko tuntubarmu
LATSA NAN
SHAFUKANMU NA SADA ZUMUNTA
Facebook.com/isyakulabari
Rubuta ra ayin ka