Wata babban Kotun daukaka kara abirnin Abuja Najeriya ta jaddada hukuncin da wata Kotu ta yanke wa Maryam Sanda bayan ta same ta da laifin kashe mijinta Bilyamin Muhammed.
Gwamnatin tarayyar Najeriya ta gurfanarda Maryam Sanda a gaban Kotu bisa tuhumar kashe mijinta Bilyamin dan gidan tsohon shugaban jam'iyar PDP ta kasa bayan wani hargitsin cikin gida da ya auku tsakanin Maryam da Bilyamin wanda ake zargin Maryam ta yi amfani da wuka ta kashe Bilyamin. a 2017.
Kotu ta yanke wa Maryam hukuncin kisa ta hanyar ratayewa har sai ta mutu bayan Kotu ta kamata da laifin tuhumar da ake yi mata.
Sai dai Maryam ta daukaka kara zuwa Kotun daukaka kara, wadda ta jaddada hukuncin Kotu na baya kan hukuncin kisa ga Maryam Sanda ta hanyar ratayewa.
https://chat.whatsapp.com/
Domin aiko labari, shawara ko tuntubarmu
LATSA NAN
SHAFUKANMU NA SADA ZUMUNTA
Facebook.com/isyakulabari