Budurwa ta kulle kofa daga waje ta banka wuta a dakin da saurayinta da maifiyarsa ke ciki


Wata yarinya ta banka wuta a gidan da saurayinta mai suna Jude yake  ciki tare da mahaifiyarsa da yaro mai shekara biyu da karfe 1:30 na dare a Gboko ta kudu a jihar Benue ranar 7 ga watan Disamba. 

Saurayinta ya ce ya fasa aurenta saboda halayenta na rashin ragowa gareshi da mahaifiyarsa. Bisa wannan dalili ne yarinyar ta dauki wannan mataki kasancewa ya ce ta kwashe kayanta ta fice ta bar masa gidansa.


Rahotanni sun ce da dare, sai yarinyar ta dawo tare da wasu mutum uku a kan babur, suka yage net na sauro da ke tagar dakin, sai suka zuba wani abu da ake zargin cewa fetur ne, daga bisani sai yarinyar ta kyasta ashana ta jefa ta taga, nan take wuta ta kama yayin da saurayinta Jude tare da mahaifiyarsa da yaro mai shekar uku suka kama da wuta.


Rahotun ya kara da cewa daga bisani yarinyar ta hau babur da suka zo da shi suka yi tafiyarsu. Ihu da Jude ya yi ta yi ya ankarar da jama'a da suka zo suka balle kofar daki, kasancewa an gano yarinyar ta kulle kofar da makulli daga waje kafin ta kyasata ashana ta jefa a dakin.


An ceto Jude, mahaifiyarsa da yaro da kuna a jikinsu. Sai dai kuna da ke jikin Jude ta fi tsananta, kuma an garzaya zuwa Asibiti da shi domin samun kulawan Likitoci.


Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp
https://chat.whatsapp.com/J9zhUeQqg52KIxyFnYByJN

Domin aiko labari, shawara ko tuntubarmu
LATSA NAN

SHAFUKANMU NA SADA ZUMUNTA

Facebook.com/isyakulabari


Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN