Type Here to Get Search Results !

Zaben Amurka: An kara yawan masu tsaron lafiyar Joe Biden a zaton lashe zaben shugaban kasa


An tura karin jami'an sirri da ke kare lafiyan shugaban kasar Amurka zuwa gidan dan takaran shugaban kasa a jam'iyar Democrat Joe Biden a Wilmington, da ke Delaware, yayin da ake kyautata zaton zai lashe zaben shugaban kasar Amurka.

CNN ta labarta cewa an kara yawan masu tsaron lafiya na Secret Service zuwa gidan Joe Biden domin kare lafiyarsa da na iyalinsa ranar Alhamis.

Kazalika Shahara Reporters ta ruwaito cewa Delaware News Journal ta labarta cewa an dakatar da zaiga zirgan jiragen sama da ke bi ta sararin samaniyar gidan Joe Biden da ke garin Wilmington



Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp
https://chat.whatsapp.com/J9zhUeQqg52KIxyFnYByJN

Domin aiko labari, shawara ko tuntubarmu
LATSA NAN

SHAFUKANMU NA SADA ZUMUNTA

Facebook.com/isyakulabari


Post a Comment

0 Comments
* Please Don't Spam Here. All the Comments are Reviewed by Admin.

Top Post Ad

Below Post Ad

Hollywood Movies