Nasarar tsaro a Katsina: Manyan yan bindiga 2 sun tuba sun mika wuya ga Gwamna Masari


Gwamna Aminu Bello Masari na jihar Katsina ya karbi manyan yan bindiga biyu da suka tuba a gidan Gwamnatin jihar Katsina. Sale Turwa da Muhammed Sani Maidaji sun tuba kuma suka mika makamansu ga Gwamnati.

Sahara Reporters ta ruwaito cewa Kwamishinan yansandan jihar Katsina Aminu Baba da takwarorinsa na Briged na 17 na soji da ke Katsina, Daraktan DSS da Kwamandan NSCDC na jihar Katsina ne suka gabatar wa Gwamna Masari da tubabbun yan bindigan da suka dade suna addaban jihar.


Kwamishinan yansandan jihar Katsina ya ce manyan jami'an tsaron jihar sun bukaci Gwamna Masarai ya duba nadama da tuba da yan bindigan suka yi kuma ya yafe masu domin su zama mutane na gari a cikin al'umma.

Ya ce wannan babban nasara ce wajen yaki da yan bindiga kuma Gwamnati a shirye take domin yafe wa tubabbun yan bindiga da suka gabatar da kansu.


Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp
https://chat.whatsapp.com/J9zhUeQqg52KIxyFnYByJN

Domin aiko labari, shawara ko tuntubarmu
LATSA NAN

SHAFUKANMU NA SADA ZUMUNTA

Facebook.com/isyakulabari


Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN