Najeriya ta fi tsiyacewa a mulkin Buhari— Cewar Bankin Duniya


Najeriya ta faɗa matsin tattalin arziƙi mafi muni a cikin shekara 30.

Wasu bayanai da Hukumar Ƙididdiga ta Najeriya, NBS ta fitar ranar Asabar sun ce Najeriya ta samu komaɗar tattalin arziƙi da kaso 3.62% a third quarter of 2020, a cewar jaridar Intanet, TheCable.


Wannan shi ne karewar Ma’aunin Tattalin Arziƙi, GDP na biyu tun karewar tattalin arziƙi ta 2016. Jimillar haɓakar GDP a watanni taran farko na 2020 ya tsaya a -2.48 cikin ɗari.

Rabon da Najeriya ta samu irin wannan karyewar GDP tun a 1987, lokacin da GDPn ya yi ƙasa da kaso 10.8 cikin ɗari.

Alƙaluman da Bankin Duniya da NBS suka fitar, waɗanda jaridar TheCable ta bibiya sun ce wannan shi ne komaɗar tattalin arziƙi ta biyu da Najeriya ta samu a mulkin Shugaba Muhammadu Buhari na farar hula— kuma ta huɗu a matsayin Shugaban Mulkin Soja.

Source:: labarai24


Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp
https://chat.whatsapp.com/J9zhUeQqg52KIxyFnYByJN

Domin aiko labari, shawara ko tuntubarmu
LATSA NAN

SHAFUKANMU NA SADA ZUMUNTA

Facebook.com/isyakulabari


Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN