Bacewar mazakuta: Hotunan yadda fusatattun matasa suka banka wuta a wajen bauta


Fusatattun matasa a garin Daudu na jihar Benue sun banka wuta a wani Mujami'a Divine Shadow Church,mallakin Malamin addini Joshua Uhembe ranar Talata 3 ga watan Nuwamba  bayan sun zarge shi da kitsa sace Mazakutar maza a karamar hukumar Guma.

Wannan yana faruwa ne kwana uku bayan matasa a garin Guma sun yi zanga zanga dangane da zargin bacewar mazakutan mutane a garin.


Kazalika matasan sun zargi Malamin addini Uhembe da shugaban Mujami'an Noah Saka da sace mazakutar matasa bakwai a garin Daudu.



Sai dai wata majiya ta sada zumunta ta ce Malamin addini Uhembe bai halarci taron da Dattijan garin suka shirya kan lamarin ba, sakamakon haka matasa suka harzuka suka banka wa Mujami'ansa wuta.


Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp
https://chat.whatsapp.com/J9zhUeQqg52KIxyFnYByJN

Domin aiko labari, shawara ko tuntubarmu
LATSA NAN

SHAFUKANMU NA SADA ZUMUNTA

Facebook.com/isyakulabari


Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN