Wani saurayi mai shekara 20 ya yi wa yarinya mai shekara 13 fyaden fitan hankali a unguwar Wadata da ke birnin Makurdi a jihar Benue, kamar yadda Igbere TV ta labarta.
Sakamakon haka jini ya yi ta zubu wa yarinyar ba kakkautawa, lamari da ya jefa rayuwarta cikin hadari.
Yansanda sun kama wanda ya yi mata wannan aiki mai suna Ali Usman, amma wani dan gwagwarmaya mai suna Ukan Kurugh ya yi zargin cewa ana matsa wa iyayen yarinyar cewa su yafe, saboda basu da zarafin shigar da kara a Kotu.
Mr Kurugh ya yi zargin cewa, ranar Lahadi 4 ga watan Oktoba, wanda ake zargi ya bukaci yarinyar ta kawo masa abinci a kofar dakinsa, isarta ke da wuya sai ya jawota da karfi kuma ya yi mata fyade. Ya ce ihu da ta yi ta yi ne ya sa makwabta suka ji, kuma suka kawo mata dauki, bayan sun sameta a sume.
KALLI YADDA SABON SARKIN ZAZZAU YA SHIGA FADA LATSA NAN
https://chat.whatsapp.com/
Domin aiko labari, shawara ko tuntubarmu
LATSA NAN
SHAFUKANMU NA SADA ZUMUNTA
Facebook.com/isyakulabari
Domin samun sassauka, ingattacciya kuma kwakkwarar DATA ta MTN, latsa nan https://chat.whatsapp.com/