Yansandan jihar Anambra sun kama wani matashi mai shekara 21 mai suna Onyeamachi Mmaju bisa zargin kashe mai gidan haya da yake ciki mai suna Nonso Oyikoba, dan shekara 35 a garin Ogidi Ani-Etiti da ke karamar hukumar Idemili na Arewa ranar Talata 6 ga watan Oktoba.
Rahotanni sun ce mai gidan hayan Nonso, ya kalubalanci mai haya a gidansa Onyeamachi cewa yana yawan shigowa da mata barkatai a gidan, ya kuma bukaci ya daina. Amma daga bisani sai rigima ya kaure, har mai haya Onyeamachi ya dauko wuka ya daba wa mai gidan haya a bayansa a wurare da dama.
Daga bisani mai gidan haya ya mutu kamar yadda Kakakin hukumar yansanda na jihar Haruna Muhammed ya tabbatar. Yanzu haka dan haya yana fuskantar bincike a sashen SCIID a Shelkwatar yansandan jihar Anambra.
https://chat.whatsapp.com/
Domin aiko labari, shawara ko tuntubarmu
LATSA NAN
SHAFUKANMU NA SADA ZUMUNTA
Facebook.com/isyakulabari
Domin samun sassauka, ingattacciya kuma kwakkwarar DATA ta MTN, latsa nan https://chat.whatsapp.com/