Yansandan jihar Niger sun kama mutum hudu da Kwarangwam kan dan adam bisa zargin tsafi a Kauyen Sabon Pegi da ke jihar ranar 3 ga watan Oktoba.
Kakakin yan sandan jihar Niger Abidoun Wasiu, ya ce wadanda aka kama su ne Alhaji Suleiman Abubakar mai shekara 50, Babuga Mamman dan shekar 42yrs, Abdullahi Dogo mai shekara 30 da Abubakar Abdullahi dan shekara 31, dukkansu yan Kauyen Sabon Pegi a karamar hukumar Mashegu.
Kakakin yansanda Wasiu,ya ce binciken farko ya nuna cewa wadanda aka kama sun tone Kabari kuma suka sare kan Gawa da aka binne a Makabartar Kauyen Kanti a karamar hukumar Ibbi Mashegu ranar 3 ga watan Oktoba da karfe 8 na dare.
Ya ce wadanda aka kama sun gaya wa yansanda lokacin bincike cewa, wani mai suna Nasiru dan garin Koko a jihar Kebbi, da Muhammadu dan garin Sabon Pegin ne suka yi alkawarin cewa zasu basu Naira Miliyan biyu idan suka samo masu kan dan adam.
https://chat.whatsapp.com/
Domin aiko labari, shawara ko tuntubarmu
LATSA NAN
SHAFUKANMU NA SADA ZUMUNTA
Facebook.com/isyakulabari
Domin samun sassauka, ingattacciya kuma kwakkwarar DATA ta MTN, latsa nan https://chat.whatsapp.com/