An kama mutum hudu da sukan tone kabari suka sare kan gawa don tsafi a jihar Niger


Yansandan jihar Niger sun kama mutum hudu da Kwarangwam kan dan adam bisa zargin tsafi a Kauyen Sabon Pegi da ke jihar ranar 3 ga watan Oktoba.

Kakakin yan sandan jihar Niger Abidoun Wasiu, ya ce wadanda aka kama su ne Alhaji Suleiman Abubakar mai shekara 50, Babuga Mamman  dan shekar 42yrs, Abdullahi Dogo mai shekara 30 da Abubakar Abdullahi dan shekara 31, dukkansu yan Kauyen  Sabon Pegi a karamar hukumar Mashegu.

Kakakin yansanda Wasiu,ya ce binciken farko ya nuna cewa wadanda aka kama sun tone Kabari kuma suka sare kan Gawa da aka binne a Makabartar Kauyen Kanti a karamar hukumar Ibbi Mashegu ranar 3 ga watan Oktoba da karfe 8 na dare.

Ya ce wadanda aka kama sun gaya wa yansanda lokacin bincike cewa, wani mai suna Nasiru dan garin Koko a jihar Kebbi, da Muhammadu  dan garin Sabon Pegin ne suka yi alkawarin cewa zasu basu Naira Miliyan biyu idan suka samo masu kan dan adam.


Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp
https://chat.whatsapp.com/JKBP5KgalYg3iQRBQoFVAE

Domin aiko labari, shawara ko tuntubarmu
LATSA NAN

SHAFUKANMU NA SADA ZUMUNTA

Facebook.com/isyakulabari


Domin samun sassauka, ingattacciya kuma kwakkwarar DATA ta MTN, latsa nan https://chat.whatsapp.com/L4xvcwRGM496Eep5J53zXt

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN