An kashe mutum ɗaya an kuma yi garkuwa da wasu bakwai a lokacin da ƴan bindiga suka kai hari garin Wasagu da ke ƙaramar hukumar Danko Wasagu na jihar Kebbi.
Yan bindigan sun afka garin na Wasugu a daren ranar Lahadi inda suka rika buɗe wa gidaje da mutane wuta. Wani ganau, da ya yi magana da SaharaReporters ya ce mutum uku sun jikkata sakamakon harin. "Sun afka garin misalin ƙarfe 7 na dare suka fara harbe-harbe, mutum uku sun samu munanan rauni.
"Ɗaya daga cikin mutane ukun ya mutu yayin da sauran biyun sunan can suna karɓar magani a Cibiyar Lafiya ta Wasugu. "Yan bindigan sun yi awon gaba da wasu mutane a garin mu yayin da wasu suka ruga gidajensu suka rufe kofofi.
"Bayan harin, mun gano cewa sun sace mutane biyar," a cewar wani mazaunin garin Aliyu. Ya ce duk da cewa a yanzu an samu lafiya a garin, mutane da dama suna zaman fargaba ne.
Ya ƙara da cewa har yanzu ƴan bindigan ba su tuntuɓi iyalan wadanda suka sace ba kan batun biyan kudin fansa. A wani labarin daban da Legit.ng ta wallafa, mutane da dama sun bace sakamakon fadawa cikin rafin Epe da wata mota ta yi daga gadar Berger a jihar Legas.
The Punch ta ruwaito cewa lamarin ya faru ne a daren ranar Juma'a 25 ga watan Satumban 2020.
Source: Legit
https://chat.whatsapp.com/
Domin aiko labari, shawara ko tuntubarmu
LATSA NAN
SHAFUKANMU NA SADA ZUMUNTA
Facebook.com/isyakulabari
Domin samun sassauka, ingattacciya kuma kwakkwarar DATA ta MTN, latsa nan https://chat.whatsapp.com/