Gwamna Bagudu ya kaddamar da rigakafin cutar haukan Kare kyauta a jihar Kebbi


Gwamna Abubakar Atiku Bagudu ya kaddamar da allurar rigakafin cutar haukar Kare kyauta a fadin jihar Kebbi a garin Birnin kebbi ranar Litinin.


Wannan ya zo daidai da ranar cutar haukan Kare na duniya wanda aka gudanar ranar Litinin 28 ga watan Satumba a babban dakin taro na shugaban kasa da ke Birnin kebbi.


Gwamna Bagudu ya ce cutar haukan Kare ana iya daukarta daga Kare, ya kalubalanci masana lafiyan dabbobi su samar da magani da kuma rigakafin cutar domin a kawar da ita gaba daya.


Kawmishinan lafiyar dabbobi da albarkatun kifi na jihar Kebbi Alhaji Aminu Garba Dandiga, ya ce Ma'aikatarsa karkashin Gwamnatin jihar Kebbi ta yi wa Karnuka 17,200 rigakafin cutar Kare, daga cikin adadin Karnuka 40,000 da ake da su a fadin jihar Kebbi.

 

Shugaban majalisar harkokin kula da lafiyar dabbobi na Najeriya AIG, Aishatu Ababakar-Baju, ta ce dubban mutane da dabbobi ne ke mutuwa a fadin Duniya a kullum, sakamakon cutar haukan dabbobi, duk da cewa ana iya yin rigakafin cutar kaso 100 domin kauce wa kamuwa da cutar.



Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp
https://chat.whatsapp.com/JKBP5KgalYg3iQRBQoFVAE

Domin aiko labari, shawara ko tuntubarmu
LATSA NAN

SHAFUKANMU NA SADA ZUMUNTA

Facebook.com/isyakulabari


Domin samun sassauka, ingattacciya kuma kwakkwarar DATA ta MTN, latsa nan https://chat.whatsapp.com/L4xvcwRGM496Eep5J53zXt


إرسال تعليق

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

أحدث أقدم

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN