An gurfanar da wata mata mai shekara 27 a gaban Kotun Majistare na Moretele da ke Arewa maso yammacin kasar Afrika ta Kudu bisa zargin kashe wata mata mai shekaru 30 mai suna Christiananh Ditsele.
An gurfanar da wanda ake tuhuma ne ranar Laraba 9 ga watan Satumba . Kakakin yansanda Lt.Col Amandah Funani, ya tabbatar da faruwar lamarin, ya kuma ce an kama wanda ake zargin ne ranar Litinin 7 ga watan Satumba a kauyen Cyferkuil kusa da Brits bayan ta kashe Christianah bisa zargin cin amanrta wajen yin soyayya da saurayinta.
Wanda ake zargi ta fuskanci Christianah ne a titi, ta kama ta da kokuwa, ta kayar da ita daga bisani ta caka mata wuka a kirji. An garzaya zuwa Asibitin Kutwanong da Christianah, amma Likitoci sun tabbatar da mutuwarta.
https://chat.whatsapp.com/
Domin aiko labari, shawara ko tuntubarmu
LATSA NAN
SHAFUKANMU NA SADA ZUMUNTA
Facebook.com/isyakulabari
Domin samun sassauka, ingattacciya kuma kwakkwarar DATA ta MTN, latsa nan https://chat.whatsapp.com/