Bidiyo:Yanda ‘Yansandan kasar Congo da wasu ‘yan ta’adda suka kwace wani ginin ofishin jakadancin Najeriya a kasar


Wasu ‘yanzanda bisa rakiyar ‘yan ta’adda a kasar Kongo sun kwacewa ofishin jakadancin Najeriya dake kasar wani gini inda suka kori ma’aikatan ciki da kuma kwace musu kayan amfaninsu.

 

Ma’aikatan Ofishin jakadancin Najeriya a kasar na cikin gidan inda wata mata me suna Hajiya Khadija bisa rakiyar ‘yansanda da wasu ‘yan daba suka shiga gidan da wata takardar Kotu suka kori daya daga cikin ma’aikacin ofishin jakadancin Najeeiyar me suna Kazeem suka kuma kwace masa kayan aikinsa, zuwa yanzu dai a Ofishinsa yake bacci, kamar yanda Sahara Reporters ta bayyana.

 

Iyalan Jean Claude Okito dake kasar sun yi ikirarin cewa Najeriya na amfani da ginin wanda mallakinsu ne ba bisa ka’ida ba.John Obi wanda shugaban ‘yan Najeriya ne dake zaune a kasar Congo yace wannan abin kunyane ga Najeriya inda ya nemi majalisa ta gayyaci Ministan harkokin kasashen waje dan jin ba’asi akan lamarin.

 

hutudole


Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp
https://chat.whatsapp.com/JKBP5KgalYg3iQRBQoFVAE

Domin aiko labari, shawara ko tuntubarmu
LATSA NAN

SHAFUKANMU NA SADA ZUMUNTA

Facebook.com/isyakulabari


Domin samun sassauka, ingattacciya kuma kwakkwarar DATA ta MTN, latsa nan https://chat.whatsapp.com/L4xvcwRGM496Eep5J53zXt

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN