Rundunar yansandan jihar Sokoto ta kama wani Sajen na yansanda mai suna Bello Garba, bisa zargin bindige mutum daya har lahira tyare da raunata mutum uku a birnin Sokoto ranar Juma'a 25 ga watan Satumba.
Kakakin rundunar yansandan jihar Sokoto ASP Muhammad Sadiq, ya ce, dansandan ya harbe wani saurayi mai shekara 25 mai suna Aminu Abdulrahman, ya kuma raunata Junaidu Abu da Babangida Muhammed tare da Awaisu Alti.
Ya ce wadanda lamarin ya rutsa da su suna raba kudin da Gwamna Aminu Tambuwal na jihar Sokoto ya basu ne domin tunawa da cikan Najeriya shekara 60 da samun yanci a Masallacin Juma'a na Sultan Bello
https://chat.whatsapp.com/
Domin aiko labari, shawara ko tuntubarmu
LATSA NAN
SHAFUKANMU NA SADA ZUMUNTA
Facebook.com/isyakulabari
Domin samun sassauka, ingattacciya kuma kwakkwarar DATA ta MTN, latsa nan https://chat.whatsapp.com/