Wasu sabbin Rahotanni sun bayyana cewa kasar China na takurawa musulman
Uighur dake yakin Xinjiang yin tsarin haihuwa ba tare da son ransu ba.
Wani
rahoto dag Daily Mail ya ruwaito wata mata, Zumret Dawud inda ta
bayyana damuwa da cewa taje gurin Likita ya dubata, bayan an dubata
kawai sai taji ashe ya daure mata mahaifane bata iya sake haihuwa.
Tace ta ji bacin rai sosai dan ta so ta sake samun da Namiji. Amma gashi yanzu ba dama.Rahoton
ya kuma cewa ana tursasawa musulman Uighur cin Naman Alade a bikin
Dragon Festival da ake duk shekara wanda bikine na masu bautar gumaka da
shima ake tursasawa musulman halarta.
Rahoton da kungiyar kabilar Uighur dake kasar Jamus suka fitar yace a baya kasar China ta wa musulman kabilar kisan kare dangi.A cewar sanarwar duk wanda yaki yadda da sharuddan cin Naman Alade ana kaishi sansanin horo.
Hutudole
DAGA ISYAKU.COM
https://chat.whatsapp.com/CSYKJgAmLEF4s1dle0Ug6J
Domin aiko labari, shawara ko tuntubarmu
LATSA NAN
SHAFUKANMU NA SADA ZUMUNTA
Facebook.com/isyakulabari